August 25, 2023

Za a kara bullo da hanyoyin karfafa ilimin yara masu bukata ta musamman a jihar Kaduna

Ma’aikatar ilimi ta jihar Kaduna ta tabbatar da aniyarta ta shigo da yara masu bukata ta musamman cikin shirye-shiryenta na tallafin ilimi tun daga tushe domin ganin cewa sun kasance masu bayar da gudummawa ga dukkan fannonin ci gaban kasar.

Babbar jami’ar mai lura da sashen fadada tallafin ilimi ga yara na hukumar ilimi ta  karamar hukumar Jema’a Mrs Josephine Paul Ekpo ce ta tabbatar da hakan lokacin da ta ziyarci wata cibiyar bayar da horon jarrabawar shiga sabbin aji wanda aka shiryawa wasu yara masu bukata ta musamman a yankin karamar hukumar.

Madam Josephine Paul ta ce, sau tari dai gwamnatoci da wasu kungiyoyin bada tallafin ilimi na kasa da kasa da suke Najeriya su kan fi mayar da hankali ne ga ilimin yaran da suke da koshin lafiya, ba tare da la’akari da sauran yara da suka gamu da wata matsala a fannin lafiyar jiki ba.

Ta ce, a sakamakon hakan ne gwamnatin jihar ta Kaduna ta hannun hukumomin ilimi na kananan hukumomin jihar ta bijiro da tsarin tallafawa ilimi irin wadannan yara, domin dai ana samun masu kaifin basira a cikinsu da gwamnati da al’ummar za su iya amfana.

 

©cri

SHARE:
Labaran Duniya 0 Replies to “Za a kara bullo da hanyoyin karfafa ilimin yara masu bukata ta musamman a jihar Kaduna”