September 4, 2023

Tabarbarewar tsaro ya janyo rufe kasuwannin dabbobin guda 8 a jihar Zamfara

Gwamnatin jihar Zamfara ta sanar da rufe wasu manyan kasuwanni 8 da ake hada-hadar cinikin dabbobi, biyo bayan ci gaba da tabarbarewar sha’anin tsaro a jihar.

Kwamishinan yada labaran jihar Alhaji Mannir Mu’azu Haidara ne ya sanar da hakan jiya Lahadi 3 ga wata cikin wata sanarwar da aka rabawa manema labarai, inda ya ce, matakin na wucin gadi ne wanda kuma ya shafi kasuwannin dake kananan hukumomi 5 kawai.

Kananan hukumomin dai sun hada da Anka, Tsafe, Maru, Zurmi da kuma Bukkuyim wadanda su ne suke da manyan kasuwannin dabbobi a jihar ta Zamfara.

Ko da a ranar Juma’ar da ta gabata sai da gwamnan jihar ta Zamfara Alhaji Dauda Lawan ya fito fili ya koka ainun kan yadda al’amuran tsaro a jihar ke kara tabarbarewa.

A jawabin da ya gabatar yayin wani taron wa’azin addinin musulunci da ma’aikatar al’amuran addini ta jihar ta shirya a Gusau, fadar gwamnatin jihar, gwamna Dauda Lawan ya yi kira ga malaman addini da ’yan siyasar jihar da su hada kai wajen gudanar da addu’o’in dorewar zaman lafiya a jihar Zamfara.

“Lokacin da na amshi wannan mulki, na fahimci matsalolin dake fuskantar wannan jihar tamu, a ta ko’ina muna da matsaloli, yau dai tsaro ya addabi kowa. Yau mun wayi gari tafiya da rana ma tana kusan gagararmu, sannan yau idan muka yi la’akari da matsayinmu a Zamfara da yadda muke da imani da yadda muka sa addini a gabanmu, amma kuma yau Allah ya jarabce mu da masifu iri-iri. Yau muna cikin talauci, muna cikin ukubar tsaro, yunwa ta yi yawa, yaran mu ba sa iya zuwa makaranta, ba ka da lafiya ba za ka iya zuwa asibiti a ba ka magani ba.”

 

©Cri

SHARE:
Labaran Duniya 0 Replies to “Tabarbarewar tsaro ya janyo rufe kasuwannin dabbobin guda 8 a jihar Zamfara”