January 16, 2023

Ofishin UN: Mutane Fiye Da Miliya 15 Suna Bukatar Agajin Jin Kai A Kasar Siriya

Ofishin Majalisar Dinkin Duniya a kasar Siriya ya jaddada bukatar aikewa da kayayyakin jin kai zuwa kasar ta Siriya

Mataimakiyar wakilin babban sakataren Majalisar Dinkin Duniya a kasar Siriya Najat Rushdi ta bukaci mambobin Hukumomin da suke gudanar da ayyukan jin kai a duniya da su ci gaba da bayar da goyon baya ga al’ummar kasar ta Siriya, yayin da adadin masu bukatar agaji jin kan dan Adam suke karuwa a kasar.

Madam Rushdi ta jaddada cewa: Akwai bukatar a gaggauta samar da karin kudade ga kasar ta Siriya, musamman ganin cewa, akwai mutane kimanin miliyan 15.3 da suke bukatar agajin jin kai, kuma ana sa ran adadin zai karu.

SHARE:
Labaran Duniya 0 Replies to “Ofishin UN: Mutane Fiye Da Miliya 15 Suna Bukatar Agajin Jin Kai A Kasar Siriya”