February 8, 2023
Najeriya ta kama hanyar cimma muradun kasar Saudiya na 2030 wajen amfani da fasahar zamani a harkokin aikin hajji

Najeriya ta kama hanyar cimma muradun kasar Saudiya na 2030 wajen amfani da fasahar zamani a harkokin aikin hajji
A ranar talata 7 ga wata hukumar aikin hajji a tarayyar Najeriya ta kaddamar da wata cibiyar bayar da horo ga ma’aikatanta da na sauran kamfanonin hada-hadar aikin hajji dake kasar, kan amfani da fasahar zamani wajen saukaka harkokin da suka shafi shirye-shiryen aikin hajji da Umra.
Shugaban hukumar Alhaji Zikrullah Hassan shi ne ya jagoranci bude cibiyar a birnin Abuja.
Daga tarayyar Najeriya wakilinmu Garba Abdullahi Bagwai ya aiko mana da rahoto.