January 15, 2023

Kamfanin hakowa da sarrafa albarkatun man fetur na Najeriya NNPCL, ya bayyana cewa cikin watan Maris din 2023 ne za a fara aikin hako danyen man fetur a Nassarawa.
Shugaban Kamfanin Mele Kyari ne ya bayyana hakan a wani sako ta shafin Tuwita, inda ya ce hakan ci gaba ne da aikin hakon mai da nufin samar da rijiyar mai ta farko a jihar ta arewacin Najeriya.
Ya shaida hakan a lokacin da yake karbar bakuncin tawagar fitattun yan asalin jihar ta Nassarawa, karkashin jagorancin Gwamnan jihar, Injiniya Abdullahi Sule a ofishin kamfanin da ke Abuja, babban birnin kasar.
Gano arzikin man a Nassarawa ya zo ne kusan wata biyar bayan da NNPC ya soma aikin hako mai a yankin Kolmani, da ke tsakanin jihohin Bauchi da Gombe.